< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Pour la fin, pour les fils de Coré, psaume. Nations, battez toutes des mains: poussez des cris de joie vers Dieu, avec une voix d’exultation,
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Parce que le Seigneur est très élevé et terrible: c’est un grand roi sur toute la terre.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Il nous a assujetti des peuples, et a mis des nations sous nos pieds.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Il a choisi en nous son héritage, la beauté de Jacob qu’il a aimée.
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Dieu est monté au milieu des acclamations de joie, et le Seigneur au son de la trompette.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Chantez notre Dieu, chantez: chantez notre Roi, chantez.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Parce que le roi de toute la terre est Dieu: chantez avec sagesse.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Dieu régnera sur les nations: Dieu est assis sur son trône saint.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Des princes de peuples se sont réunis au Dieu d’Abraham; parce que les dieux puissants de la terre ont été extraordinairement élevés.

< Zabura 47 >