< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Au chef des chantres. Par les fils de Coré. Psaume. Vous tous, ô peuples, battez des mains; faites retentir des cris de joie en l’honneur de Dieu!
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Car l’Eternel est élevé, redoutable, un grand roi sur toute la terre.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Il a soumis des nations à notre empire, jeté des peuples sous nos pieds.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Il a choisi pour nous notre héritage, l’orgueil de Jacob qu’il affectionne. (Sélah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Dieu s’élève dans les hauteurs parmi les acclamations, l’Eternel, au son de la trompette.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Chantez Dieu, chantez! Chantez notre roi, chantez!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Car Dieu est roi de toute la terre: entonnez un solennel cantique.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Dieu règne sur les peuples, Dieu siège sur son trône de sainteté.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Que les plus nobles d’entre les nations s’assemblent le peuple du Dieu d’Abraham! Car de Dieu relèvent ceux qui sont les boucliers de la terre: il est souverainement élevé.