< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
To the Overseer. — By sons of Korah. A Psalm. All ye peoples, clap the hand, Shout to God with a voice of singing,
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For Jehovah Most High [is] fearful, A great king over all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He leadeth peoples under us, and nations under our feet.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He doth choose for us our inheritance, The excellency of Jacob that He loves. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God hath gone up with a shout, Jehovah with the sound of a trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Praise God — praise — give praise to our king, praise.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For king of all the earth [is] God, Give praise, O understanding one.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God hath reigned over nations, God hath sat on His holy throne,
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Nobles of peoples have been gathered, [With] the people of the God of Abraham, For to God [are] the shields of earth, Greatly hath He been exalted!

< Zabura 47 >