< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
For the Chief Musician; a Psalm of the sons of Korah. O clap your hands, all ye peoples; shout unto God with the voice of triumph.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For the LORD Most High is terrible; he is a great King over all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He shall subdue the peoples under us, and the nations under our feet.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He shall choose our inheritance for us, the excellency of Jacob whom he loved. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God is gone up with a shout, the LORD with the sound of a trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Sing praises to God, sing praises: sing praises unto our King, sing praises.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For God is the King of all the earth: sing ye praises with understanding.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God reigneth over the nations: God sitteth upon his holy throne.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
The princes of the peoples are gathered together [to be] the people of the God of Abraham: for the shields of the earth belong unto God; he is greatly exalted.

< Zabura 47 >