< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
“For the leader of the music. A psalm of the sons of Korah.” O clap your hands, all ye nations! Shout unto God with the voice of triumph!
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For terrible is Jehovah, the Most High, The great king over all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He hath subdued nations under us, And kingdoms under our feet;
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He hath chosen for us an inheritance, The glory of Jacob, whom he loved. (Pause)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God goeth up with a shout; Jehovah with the sound of the trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Sing praises to God, sing praises! Sing praises to our king, sing praises!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For God is king of all the earth; Sing to him hymns of praise!
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God reigneth over the nations; God sitteth upon his holy throne.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
The princes of the nations gather themselves together To the people of the God of Abraham; For the mighty of the earth belong to God; He is supremely exalted.

< Zabura 47 >