< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
To the chief Musician, A Psalm for the sons of Korah. O clap your hands, all ye people; shout unto God with the voice of triumph.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For the LORD most high [is] terrible; [he is] a great King over all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He shall subdue the people under us, and the nations under our feet.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He shall choose our inheritance for us, the excellency of Jacob whom he loved. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God is gone up with a shout, the LORD with the sound of a trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Sing praises to God, sing praises: sing praises unto our King, sing praises.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For God [is] the King of all the earth: sing ye praises with understanding.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God reigneth over the heathen: God sitteth upon the throne of his holiness.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
The princes of the people are gathered together, [even] the people of the God of Abraham: for the shields of the earth [belong] unto God: he is greatly exalted.