< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
For the music director. A psalm of the sons of Korah. Everyone, clap your hands! Shout with joy to the Lord!
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For the Lord Most High is awe-inspiring; he is the great King of all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He subdues other peoples under us; he puts nations under our feet.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He chose the land for us to own; the proud possession of Jacob's descendants whom he loves. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God ascends his throne with a great shout, the Lord is accompanied by the sound of the trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Sing praises to God, sing praises; sing praises to our King, sing praises!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For God is King of all the earth; sing praises with a psalm!
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God rules over the nations; he sits on his holy throne.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
The rulers of the nations gather together with the people of the God of Abraham, for the defenders of the earth belong to God. He is highly honored everywhere.

< Zabura 47 >