< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
O clap your hands, all ye peoples. Shout to God with the voice of triumph.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
For Jehovah Most High is awesome. He is a great King over all the earth.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
He subdues peoples under us, and nations under our feet.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
He chooses our inheritance for us, the glory of Jacob whom he loved. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
God has gone up with a shout, Jehovah with the sound of a trumpet.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Sing praise to God, sing praises. Sing praises to our King, sing praises.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
For God is the King of all the earth. Sing ye praises with understanding.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
God reigns over the nations. God sits upon his holy throne.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
The nobles of the peoples are gathered together, the people of the God of Abraham. For the shields of the earth belong to God. He is greatly exalted.

< Zabura 47 >