< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Zborovođi. Sinova Korahovih. Psalam. Narodi svi, plješćite rukama, kličite Bogu glasom radosnim.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Jer Jahve je to - svevišnji, strašan, kralj velik nad zemljom svom.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Narode je nama podložio, pogane stavio pod noge naše,
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
baštinu nam odabrao - ponos Jakova, svoga ljubimca.
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Uzlazi Bog uz klicanje, Jahve uza zvuke trublje.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Pjevajte Bogu, pjevajte, pjevajte kralju našemu, pjevajte!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Jer on je kralj nad zemljom svom, pjevajte Bogu, pjevači vrsni!
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Bog kraljuje nad narodima, stoluje Bog na svetom prijestolju.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Prvaci se pribiru poganski k narodu Boga Abrahamova. Božji su svi vlastodršci zemlje, nad svima on je uzvišen.

< Zabura 47 >