< Zabura 46 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Dios es nuestro amparo y fortaleza: socorro en las angustias hallarémos en abundancia.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Por tanto no temeremos, aunque la tierra se mude, y aunque se traspasen los montes al corazón de la mar.
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
Bramarán, turbarse han sus aguas: temblarán los montes a causa de su bravura. (Selah)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
Del río sus conductos alegrarán la ciudad de Dios, el santuario de las tiendas del Altísimo.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
Dios está en medio de ella, no será movida: Dios la ayudará en mirando la mañana.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Bramaron naciones, titubearon reinos: dio su voz, derritióse la tierra:
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
Jehová de los ejércitos es con nosotros: nuestro refugio es el Dios de Jacob. (Selah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Veníd, ved las obras de Jehová, que ha puesto asolamientos en la tierra.
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
Que hace cesar las guerras hasta los fines de la tierra; que quiebra el arco, y corta la lanza, y quema los carros en el fuego.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
Cesád, y conocéd que yo soy Dios: ensalzarme he en las naciones, ensalzarme he en la tierra.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
Jehová de los ejércitos es con nosotros: nuestro refugio es el Dios de Jacob. (Selah)