< Zabura 46 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Por el jefe de los músicos. Por los hijos de Coré. Según Alamot. Dios es nuestro refugio y nuestra fuerza, una ayuda muy presente en los problemas.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Por eso no tendremos miedo, aunque la tierra cambie, aunque las montañas se agiten en el corazón de los mares;
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
aunque sus aguas rugen y se agitan, aunque las montañas tiemblen con su hinchazón. (Selah)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
Hay un río cuyas corrientes alegran la ciudad de Dios, el lugar santo de las tiendas del Altísimo.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
Dios está dentro de ella. Ella no será movida. Dios la ayudará al amanecer.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Las naciones se enfurecieron. Los reinos se conmovieron. Levantó la voz y la tierra se derritió.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
El Señor de los Ejércitos está con nosotros. El Dios de Jacob es nuestro refugio. (Selah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Vengan, vean las obras de Yahvé, qué desolaciones ha hecho en la tierra.
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
Hace cesar las guerras hasta el fin de la tierra. Rompe el arco y destroza la lanza. Quema los carros en el fuego.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
“Estad tranquilos y sabed que yo soy Dios. Seré exaltado entre las naciones. Seré exaltado en la tierra”.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
Yahvéde los Ejércitos está con nosotros. El Dios de Jacob es nuestro refugio. (Selah)

< Zabura 46 >