< Zabura 46 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Para el director del coro, por los hijos de Coré. Según e canto de Alamot. Dios es nuestra protección y nuestra fuerza; siempre listo para ayudar cuando vienen los problemas.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Así que no tendremos miedo aunque la tierra tiemble, aunque las montañas caigan hacia el fondo de los océanos,
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
Aunque las aguas rujan y, ¡Aunque las montañas tiemblen y las aguas se levanten violentamente! (Selah)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
Un río fluye para traer felicidad a los que viven en la ciudad de Dios, la ciudad santa donde vive el Altísimo.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
Dios está en la mitad de la ciudad; y esta nunca caerá. Dios la protege con la rapidez de la luz.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Las naciones están en confusión, Los reinos colapsan. Dios levanta su voz y la tierra se estremece.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
El Señor Todopoderoso está con nosotros; El Dios de Jacob nos protege. (Selah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
¡Ven para veas lo que el Señor ha hecho! ¡Mira las cosas maravillosas que ha hecho en la tierra!
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
Él detiene guerras alrededor de todo el mundo. Aplasta ballestas; rompe lanzas; incendia los escudos.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
¡Dejen de pelear! ¡Reconozcan que yo soy Dios! Yo soy el gobernador de las naciones; Soy el gobernador de la tierra.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
El Señor todopoderoso está con nosotros; El Dios de Jacob nos protege. (Selah)

< Zabura 46 >