< Zabura 46 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
“For the leader of the music. Of, or for, the sons of Korah. To be sung in the manner, or with the voice, of virgins.” God is our refuge and strength; An ever present help in trouble.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Therefore will we not fear, though the earth be changed; Though the mountains tremble in the heart of the sea;
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
Though its waters roar and be troubled, And the mountains shake with the swelling thereof. (Pause)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
A river with its streams shall make glad the city of God, The holy dwelling-place of the Most High.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
God is the midst of her; she shall not be moved; God will help her, and that full early.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
The nations raged; kingdoms were moved; He uttered his voice, the earth melted.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The LORD of hosts is with us; The God of Jacob is our refuge. (Pause)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Come, behold the doings of the LORD; What desolations he hath made in the earth!
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
He causeth wars to cease to the end of the earth; He hath broken the bow, and snapped the spear asunder, And burned the chariots in fire.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
“Desist, and know that I am God; I will be exalted among the nations, I will be exalted throughout the earth!”
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The LORD of hosts is with us; The God of Jacob is our refuge.

< Zabura 46 >