< Zabura 46 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
For the music director by the sons of Korah. According to alamoth, a song. God is our protection and our strength; always ready to help when troubles come.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
So we will not be afraid though the earth shakes, though the mountains fall into the depths of the sea,
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
though the waters roar and foam, though the mountains tremble as the waters surge violently! (Selah)
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
A river flows to bring happiness to those in God's city, the holy place where the Most High lives.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
God is in the midst of the city; it will never fall. God protects it as soon as it is light.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Nations are in turmoil, kingdoms collapse. God raises his voice and the earth melts.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The Lord Almighty is with us; the God of Jacob protects us. (Selah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Come and see what the Lord has achieved! See the amazing things he has done on the earth!
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
He stops wars all over the world. He smashes the bow; he breaks the spear; he sets shields on fire.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
Stop fighting! Recognize I am God! I am the ruler of the nations; I am the ruler of the earth.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The Lord Almighty is with us; the God of Jacob protects us. (Selah)