< Zabura 46 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Unto the end. To the sons of Korah, for confidants. A Psalm. Our God is our refuge and strength, a helper in the tribulations that have greatly overwhelmed us.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Because of this, we will not be afraid when the earth will be turbulent and the mountains will be transferred into the heart of the sea.
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
They thundered, and the waters were stirred up among them; the mountains have been disturbed by his strength.
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
The frenzy of the river rejoices the city of God. The Most High has sanctified his tabernacle.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
God is in its midst; it will not be shaken. God will assist it in the early morning.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
The peoples have been disturbed, and the kingdoms have been bowed down. He uttered his voice: the earth has been moved.
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The Lord of hosts is with us. The God of Jacob is our supporter.
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Draw near and behold the works of the Lord: what portents he has set upon the earth,
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
carrying away wars even to the end of the earth. He will crush the bow and break the weapons, and he will burn the shield with fire.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
Be empty, and see that I am God. I will be exalted among the peoples, and I will be exalted upon the earth.
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
The Lord of hosts is with us. The God of Jacob is our supporter.