< Zabura 45 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Lili.” Na’ya’yan Kora maza. Maskil Waƙar Aure. Zuciyata ta cika da kyakkyawan kan magana yayinda nake rera ayoyina wa sarki; harshena ne alƙalamin ƙwararren marubuci.
Maskil des enfants de Coré, [qui est] un Cantique nuptial, [donné] au maitre chantre, [pour le chanter] sur Sosannim. Mon cœur médite un excellent discours, [et] j'ai dit: mes ouvrages seront pour le Roi; ma langue sera la plume d'un écrivain diligent.
2 Kai ne mafi kyau cikin mutane an kuma shafe leɓunanka da alheri, da yake Allah ya albarkace ka har abada.
Tu es plus beau qu'aucun des fils des hommes; la grâce est répandue sur tes lèvres, parce que Dieu t'a béni éternellement.
3 Ka ɗaura takobinka a gefenka, ya jarumi; ka rufe kanka da ɗaukaka da kuma daraja.
Ô Très-puissant, ceins ton épée sur ta cuisse, ta majesté et ta magnificence.
4 Cikin darajarka ka hau zuwa nasara a madadin gaskiya, tawali’u da adalci; bari hannunka na dama yă nuna ayyukan banmamaki.
Et prospère en ta magnificence; sois porté sur la parole de vérité, de débonnaireté, et de justice; et ta droite t'enseignera des choses terribles.
5 Bari kibiyoyinka masu tsini su huda zukatan abokan gāban sarki; bari al’ummai su fāɗi ƙarƙashin ƙafafunka.
Tes flèches sont aiguës, les peuples tomberont sous toi; [elles entreront] dans le cœur des ennemis du Roi.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin; sandar adalci zai zama sandar mulkinka.
Ton trône, ô Dieu! est à toujours et à perpétuité; le sceptre de ton règne est un sceptre d'équité.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai kana kuma ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya sa ka a bisa abokanka ta wurin shafe ka da man farin ciki.
Tu aimes la justice, et tu hais la méchanceté; c'est pourquoi, ô Dieu! ton Dieu t'a oint d'une huile de joie par-dessus tes compagnons.
8 Dukan rigunanka suna ƙanshin turaren mur da na aloyes, da na kashiya; daga kowace fadan da aka yi masa ado da hauren giwa kaɗe-kaɗen tsirkiya kan sa ka murna.
Ce n'est que myrrhe, aloès et casse de tous tes vêtements, [quand tu sors] des palais d'ivoire, dont ils t'ont réjoui.
9 ’Ya’yan sarki mata suna cikin matan da ake girmama; a hannun damarka kuwa ga amarya, sarauniya saye da ofir zinariya.
Des filles de Rois sont entre tes dames d'honneur; ta femme est à ta droite, parée d'or d'Ophir.
10 Ki saurara, ya ke diya, ki lura ku kuma kasa kunne, Ki manta da mutanenki da gidan mahaifinki.
Ecoute fille, et considère; rends-toi attentive, oublie ton peuple, et la maison de ton père.
11 Sarki ya cika da sha’awar kyanki; ki girmama shi, gama shi ne maigidanki.
Et le Roi mettra son affection en ta beauté; puisqu'il est ton Seigneur, prosterne-toi devant lui.
12 Diyar Taya za tă zo da kyauta, mawadata za su nemi tagomashinki.
Et la fille de Tyr, [et] les plus riches des peuples te supplieront avec des présents.
13 Gimbiya tana fada, kyakkyawa ce ainun; an saƙa rigarta da zaren zinariya.
La fille du Roi est intérieurement toute pleine de gloire; son vêtement est semé d'enchâssures d'or.
14 Cikin riguna masu ado aka kai ta wurin sarki; abokanta budurwai suna biye da ita aka kuwa kawo su gare ka.
Elle sera présentée au Roi en vêtements de broderie; et les filles qui viennent après elle, et qui sont ses compagnes, seront amenées vers toi.
15 Aka bi da su cikin farin ciki da murna; suka shiga fadan sarki.
Elles te seront présentées avec réjouissance et allégresse, [et] elles entreront au palais du Roi.
16 ’Ya’yanka maza za su maye matsayin kakanninka; za ka sa su yi mulki a duk fāɗin ƙasar.
Tes enfants seront au lieu de tes pères; tu les établiras pour Princes par toute la terre.
17 Zan sa a tuna da kai a dukan zamanai; saboda haka al’ummai za su yabe ka har abada abadin.
Je rendrai ton Nom mémorable dans tous les âges, et à cause de cela les peuples te célébreront à toujours et à perpétuité.

< Zabura 45 >