< Zabura 45 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Lili.” Na’ya’yan Kora maza. Maskil Waƙar Aure. Zuciyata ta cika da kyakkyawan kan magana yayinda nake rera ayoyina wa sarki; harshena ne alƙalamin ƙwararren marubuci.
Jusqu'à la Fin, avec chants alternés, une instruction des fils de Koré, un cantique au sujet du bien-aimé. Mon cœur a exhalé une bonne parole; je dédie mes œuvres au Roi. Ma langue est le roseau d'un scribe écrivant avec rapidité.
2 Kai ne mafi kyau cikin mutane an kuma shafe leɓunanka da alheri, da yake Allah ya albarkace ka har abada.
Tu es plus beau que les fils des hommes; la grâce est répandue sur tes lèvres. A cause de cela, Dieu t'a béni à jamais.
3 Ka ɗaura takobinka a gefenka, ya jarumi; ka rufe kanka da ɗaukaka da kuma daraja.
Ceins l'épée qui s'appuie sur ta cuisse, ô Puissant!
4 Cikin darajarka ka hau zuwa nasara a madadin gaskiya, tawali’u da adalci; bari hannunka na dama yă nuna ayyukan banmamaki.
En ta jeunesse et en ta beauté, tends ton arc, marche et prospère, et règne par l'amour de la vérité, de la douceur et de la justice, et ta droite te guidera merveilleusement.
5 Bari kibiyoyinka masu tsini su huda zukatan abokan gāban sarki; bari al’ummai su fāɗi ƙarƙashin ƙafafunka.
Tes traits sont aiguisés, ô Puissant; ils renverseront les peuples; ils perceront le cœur des ennemis du Roi.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin; sandar adalci zai zama sandar mulkinka.
Ton trône, ô mon Dieu, sera dans les siècles des siècles; ton sceptre de roi est le sceptre de la justice.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai kana kuma ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya sa ka a bisa abokanka ta wurin shafe ka da man farin ciki.
Tu aimes la justice et tu hais l'iniquité; à cause de cela, ô Dieu, ton Dieu a fait de toi son Christ; il a répondu sur toi plus que sur tes compagnons l'huile de l'allégresse.
8 Dukan rigunanka suna ƙanshin turaren mur da na aloyes, da na kashiya; daga kowace fadan da aka yi masa ado da hauren giwa kaɗe-kaɗen tsirkiya kan sa ka murna.
La myrrhe, les essences et la casse s'exhalent de tes vêtements et de tes palais d'ivoire, et, réunies en ton honneur, elles te réjouissent,
9 ’Ya’yan sarki mata suna cikin matan da ake girmama; a hannun damarka kuwa ga amarya, sarauniya saye da ofir zinariya.
Les filles des rois. La reine s'est placée à ta droite, revêtue d'un manteau d'or diversement orné.
10 Ki saurara, ya ke diya, ki lura ku kuma kasa kunne, Ki manta da mutanenki da gidan mahaifinki.
Écoute, ma fille, et vois, et incline ton oreille; oublie ton peuple et la maison de ton père;
11 Sarki ya cika da sha’awar kyanki; ki girmama shi, gama shi ne maigidanki.
Car le roi s'est épris de ta beauté, lui qui est ton seigneur:
12 Diyar Taya za tă zo da kyauta, mawadata za su nemi tagomashinki.
Et les filles de Tyr t'adoreront avec des présents; les riches du peuple de la terre prieront devant ta face.
13 Gimbiya tana fada, kyakkyawa ce ainun; an saƙa rigarta da zaren zinariya.
Toute sa gloire est comme celle de la fille du roi d'Esebon, revêtue d'une parure de franges d'or,
14 Cikin riguna masu ado aka kai ta wurin sarki; abokanta budurwai suna biye da ita aka kuwa kawo su gare ka.
Et diversement ornée. Les vierges de sa suite sont amenées au roi; ses compagnes te seront amenées.
15 Aka bi da su cikin farin ciki da murna; suka shiga fadan sarki.
Elles te seront amenées avec joie et allégresse; elles seront conduites en la demeure du Roi.
16 ’Ya’yanka maza za su maye matsayin kakanninka; za ka sa su yi mulki a duk fāɗin ƙasar.
A la place de tes frères, des fils te sont nés; tu les institueras chefs de toute la terre.
17 Zan sa a tuna da kai a dukan zamanai; saboda haka al’ummai za su yabe ka har abada abadin.
Ils se souviendront de ton nom de génération en génération; à cause de cela, les peuples te rendront grâces éternellement et dans les siècles des siècles.

< Zabura 45 >