< Zabura 45 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Lili.” Na’ya’yan Kora maza. Maskil Waƙar Aure. Zuciyata ta cika da kyakkyawan kan magana yayinda nake rera ayoyina wa sarki; harshena ne alƙalamin ƙwararren marubuci.
To the Overseer. — 'On the Lilies.' — By sons of Korah. — An Instruction. — A song of loves. My heart hath indited a good thing, I am telling my works to a king, My tongue [is] the pen of a speedy writer.
2 Kai ne mafi kyau cikin mutane an kuma shafe leɓunanka da alheri, da yake Allah ya albarkace ka har abada.
Thou hast been beautified above the sons of men, Grace hath been poured into thy lips, Therefore hath God blessed thee to the age.
3 Ka ɗaura takobinka a gefenka, ya jarumi; ka rufe kanka da ɗaukaka da kuma daraja.
Gird Thy sword upon the thigh, O mighty, Thy glory and Thy majesty!
4 Cikin darajarka ka hau zuwa nasara a madadin gaskiya, tawali’u da adalci; bari hannunka na dama yă nuna ayyukan banmamaki.
As to Thy majesty — prosper! — ride! Because of truth, and meekness — righteousness, And Thy right hand showeth Thee fearful things.
5 Bari kibiyoyinka masu tsini su huda zukatan abokan gāban sarki; bari al’ummai su fāɗi ƙarƙashin ƙafafunka.
Thine arrows [are] sharp, — Peoples fall under Thee — In the heart of the enemies of the king.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin; sandar adalci zai zama sandar mulkinka.
Thy throne, O God, [is] age-during, and for ever, A sceptre of uprightness [Is] the sceptre of Thy kingdom.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai kana kuma ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya sa ka a bisa abokanka ta wurin shafe ka da man farin ciki.
Thou hast loved righteousness and hatest wickedness, Therefore God, thy God, hath anointed thee, Oil of joy above thy companions.
8 Dukan rigunanka suna ƙanshin turaren mur da na aloyes, da na kashiya; daga kowace fadan da aka yi masa ado da hauren giwa kaɗe-kaɗen tsirkiya kan sa ka murna.
Myrrh and aloes, cassia! all thy garments, Out of palaces of ivory Stringed instruments have made thee glad.
9 ’Ya’yan sarki mata suna cikin matan da ake girmama; a hannun damarka kuwa ga amarya, sarauniya saye da ofir zinariya.
Daughters of kings [are] among thy precious ones, A queen hath stood at thy right hand, In pure gold of Ophir.
10 Ki saurara, ya ke diya, ki lura ku kuma kasa kunne, Ki manta da mutanenki da gidan mahaifinki.
Hearken, O daughter, and see, incline thine ear, And forget thy people, and thy father's house,
11 Sarki ya cika da sha’awar kyanki; ki girmama shi, gama shi ne maigidanki.
And the king doth desire thy beauty, Because he [is] thy lord — bow thyself to him,
12 Diyar Taya za tă zo da kyauta, mawadata za su nemi tagomashinki.
And the daughter of Tyre with a present, The rich of the people do appease thy face.
13 Gimbiya tana fada, kyakkyawa ce ainun; an saƙa rigarta da zaren zinariya.
All glory [is] the daughter of the king within, Of gold-embroidered work [is] her clothing.
14 Cikin riguna masu ado aka kai ta wurin sarki; abokanta budurwai suna biye da ita aka kuwa kawo su gare ka.
In divers colours she is brought to the king, Virgins — after her — her companions, Are brought to thee.
15 Aka bi da su cikin farin ciki da murna; suka shiga fadan sarki.
They are brought with joy and gladness, They come into the palace of the king.
16 ’Ya’yanka maza za su maye matsayin kakanninka; za ka sa su yi mulki a duk fāɗin ƙasar.
Instead of thy fathers are thy sons, Thou dost appoint them for princes in all the earth.
17 Zan sa a tuna da kai a dukan zamanai; saboda haka al’ummai za su yabe ka har abada abadin.
I make mention of Thy name in all generations, Therefore do peoples praise Thee, To the age, and for ever!