< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Для дириґента хору. Синів Коре́євих. Псало́м навча́льний. Боже, своїми ушима ми чули, наші батьки́ нам оповіда́ли: велике Ти ді́ло вчинив за їхніх днів, за днів старода́вніх:
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Ти вигнав пога́нів Своєю рукою, а їх осади́в, понищив народи, а їх Ти поши́рив!
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Не мече́м бо своїм вони землю посі́ли, і їхнє раме́но їм не помогло́, — а прави́ця Твоя та раме́но Твоє, та Світло обличчя Твого́, бо Ти їх уподо́бав!
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Ти Сам — Цар мій, о Боже, звели ж про спасі́ння для Якова:
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Тобою поб'ємо своїх ворогів, Ім'я́м Твоїм будемо топта́ти повсталих на нас,
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
бо я буду наді́ятися не на лу́ка свого́, і мій меч не поможе мені,
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
але Ти нас спасеш від противників наших, і наших нена́висників засоро́миш!
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Ми хва́лимось Богом щодня́, і пові́ки Ім'я́ Твоє сла́вимо, (Се́ла)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
та однак Ти покинув і нас засоро́мив, і вже не вихо́диш із нашими ві́йськами:
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Ти вчинив, що від ворога ми оберну́лись назад, а наші нена́висники грабува́ли собі наш маєток.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Ти віддав нас на по́їд, немов тих ове́чок, і нас розпоро́шив посеред наро́дів,
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Ти за бе́зцін продав Свій наро́д, і ціни́ йому не побільши́в!
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Ти нас нашим сусідам віддав на знева́гу, на нару́гу та по́сміх для наших око́лиць,
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Ти нас учинив за прислі́в'я пога́нам, і головою хита́ють наро́ди на нас.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Передо мною щоденно безче́стя моє, і сором вкриває обличчя моє, —
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
через голос того, хто лає мене й проклинає, через ворога й ме́сника.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Прийшло було все це на нас, та ми не забу́ли про Тебе, й заповіту Твого не пору́шили,
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
не вступи́лось назад наше серце, і не відхили́вся наш крок від Твоєї доро́ги!
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Хоч у місце шака́лів Ти ви́пхнув був нас, і прикрив був нас сме́ртною тінню, —
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
чи й тоді ми забули Ім'я́ Бога нашого, і руки свої простягну́ли до Бога чужого?
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Таж про те Бог дові́дається, бо Він знає тає́мності серця, —
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
що нас побива́ють за Тебе щоденно, пораховано нас, як овечок жерто́вних.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Прокинься ж, — для чо́го Ти, Господи, спиш? Пробуди́ся, — не кидай наза́вжди!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Для чо́го обличчя Своє Ти ховаєш, забуваєш про нашу недолю та нашу тісно́ту?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Бо душа наша зни́жилася аж до по́роху, а живіт наш приліг до землі.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Устань же, о По́моче наша, і ви́купи нас через милість Свою!

< Zabura 44 >