< Zabura 44 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Para el director del coro. Un salmo (masquil) de los hijos de Coré. Dios, hemos escuchado con nuestros propios oídos, nuestros antepasados nos han dicho todo lo que tú hiciste en sus épocas, mucho tiempo atrás.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Con tu poder quitaste del camino a las otras naciones, estableciste a nuestros antepasados en el lugar que les pertenecía; derrotaste a las naciones y enviaste a nuestros ancestros a ocupar la tierra que les habías prometido.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
No conquistaron la tierra con sus espadas; no fue a través de su fuerza que ganaron la victoria, fue por tu fuerza, tu poder, y tu compañía, porque los amabas.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Dios, tú eres mi rey. ¡Nos diste victorias en nombre de Jacob!
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Solo a través de ti podemos ahuyentar a nuestros enemigos. Solo en tu nombre podemos derrotar a nuestros oponentes.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
No confío en mi arco; no creo que mi espada vaya a salvarme.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
Tú eres el único que nos salva de nuestros enemigos; acabas con aquellos que nos odian.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Dios, te alabamos gozosos todo el día y alabamos tu nombre. (Selah)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Pero ahora nos has rechazado y has apartado tu gracia de nosotros; has abandonado a nuestros ejércitos.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Nos has hecho correr huyendo de nuestros enemigos, y quienes nos odian se han llevado todo lo que han querido.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Nos has entregado como una oveja que va al sacrificio; nos has escatimado en frente de las otras naciones.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Has vendido a tu propio pueblo por el precio de nada, no haciendo ni una sola queja al momento de la venta.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Te has burlado de nosotros en frente de nuestros prójimos, somos ridiculizados y burlados por todos los que están a nuestro alrededor.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Nos has vuelto un chiste para las otras naciones; sacuden con fuerza sus manos ante nosotros.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Somos humillados el día entero; escondemos nuestras cabezas por la vergüenza,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
por todos los insultos de las personas que se burlan de nosotros, porque nuestros enemigos vengativos están justo detrás de nosotros.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Todo esto nos ha pasado incluso aunque nunca te olvidamos; no hemos sido infieles a las promesas que nos has hecho.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
No nos hemos alejado de ti, ni en pensamientos, ni en acciones.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Pero tú nos aplastaste, y nos convertiste en guarida de chacales. Nos has cubierto con la oscuridad de la muerte.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si hemos olvidado el nombre de nuestro Dios, o hemos adorado a otros dioses,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
¿No lo sabría Dios, siendo que él conoce los pensamientos de todos?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Pero por tu culpa nos matan día y noche. Somos considerados solo como ovejas listas para el sacrificio.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
¡Despiértate Señor! ¿Por qué estás durmiendo? ¡Levántate! ¡No nos des la espalda por siempre!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
¿Por qué apartas tu vista de nosotros y no de tas cuenta de nuestra miseria y sufrimiento?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Caemos arruinados al polvo, nuestros cuerpos caen de cara al mugre.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
¡Levántate! ¡Ven y ayúdanos! ¡Sálvanos por la gracia de tu misericordioso amor!