< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Al maestro de coro. De los hijos de Coré. Maskil. Oímos, oh Dios, con nuestros oídos, nos contaron nuestros padres, los prodigios que hiciste en sus días, en los días antiguos.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Tú, con tu mano, expulsando pueblos gentiles, los plantaste a ellos; destruyendo naciones, a ellos los propagaste.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Pues no por su espada ocuparon la tierra, ni su brazo les dio la victoria; fue tu diestra y tu brazo, y la luz de tu rostro; porque Tú los amabas.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Tú eres mi Rey, mi Dios, Tú, el que dio la victoria a Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Por Ti batimos a nuestros enemigos; y en nombre tuyo hollamos a los que se levantaron contra nosotros.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Porque no en mi arco puse mi confianza, ni me salvó mi espada,
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
sino que Tú nos has salvado de nuestros adversarios, y has confundido a los que nos odian.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
En Dios nos gloriábamos cada día, y continuamente celebrábamos tu Nombre.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Pero ahora Tú nos has repelido y humillado; ya no sales, oh Dios, con nuestros ejércitos.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Nos hiciste ceder ante nuestros enemigos, y los que nos odian nos han saqueado como han querido.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Nos entregaste como ovejas destinadas al matadero, y nos desparramaste entre los gentiles.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Vendiste a tu pueblo sin precio, y no sacaste gran provecho de esa venta.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Nos hiciste el escarnio de nuestros vecinos, la irrisión y el ludibrio de los que nos rodean.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Nos convertiste en fábula de los gentiles, y recibimos de los pueblos meneos de cabeza.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Todo el día tengo ante los ojos mi ignominia, y la confusión cubre mi rostro,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
a los gritos del que me insulta y envilece, a la vista del enemigo, ávido de venganza.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Todo esto ha venido sobre nosotros, mas no nos hemos olvidado de Ti, ni hemos quebrantado el pacto hecho contigo.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
No volvió atrás nuestro corazón, ni nuestro paso se apartó de tu camino,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
cuando nos aplastaste en un lugar de chacales y nos cubriste con sombras de muerte.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si nos hubiéramos olvidado del nombre de nuestro Dios, extendiendo nuestras manos a un Dios extraño,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
¿no lo habría averiguado Dios, Él, que conoce los secretos del corazón?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Mas por tu causa somos ahora carneados cada día, tenidos como ovejas de matadero.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Despierta, Señor. ¿Por qué duermes? Levántate; no nos deseches para siempre.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
¿Por qué ocultas tu rostro? ¿Te olvidas de nuestra miseria y de nuestra opresión?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Agobiada hasta el polvo está nuestra alma, y nuestro cuerpo pegado a la tierra.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
¡Levántate en nuestro auxilio, líbranos por tu piedad!

< Zabura 44 >