< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Til sangmesteren; av Korahs barn; en læresalme. Gud, med våre ører har vi hørt, våre fedre har fortalt oss den gjerning du gjorde i deres dager, i fordums dager.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Du drev hedningene ut med din hånd, men dem plantet du; du ødela folkene, men dem lot du utbrede sig.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For ikke ved sitt sverd inntok de landet, og deres arm hjalp dem ikke, men din høire hånd og din arm og ditt åsyns lys; for du hadde behag i dem.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Du er min konge, Gud; byd at Jakob skal frelses!
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Ved dig skal vi nedstøte våre fiender, ved ditt navn skal vi nedtrede dem som reiser sig imot oss.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For på min bue stoler jeg ikke, og mitt sverd frelser mig ikke,
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
men du har frelst oss fra våre fiender, og våre avindsmenn har du gjort til skamme.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Gud priser vi den hele dag, og ditt navn lover vi evindelig. (Sela)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Og enda har du nu forkastet oss og latt oss bli til skamme, og du drar ikke ut med våre hærer.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Du lar oss vike tilbake for fienden, og våre avindsmenn tar sig bytte.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Du gir oss bort som får til å etes, og spreder oss iblandt hedningene.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Du selger ditt folk for intet, og du setter ikke prisen på dem høit.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Du gjør oss til hån for våre naboer, til spott og spe for dem som bor omkring oss.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Du gjør oss til et ordsprog iblandt hedningene; de ryster på hodet av oss iblandt folkene.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Hele dagen står min skam for mine øine, og blygsel dekker mitt ansikt,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
når jeg hører spotteren og håneren, når jeg ser fienden og den hevngjerrige.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Alt dette er kommet over oss, enda vi ikke har glemt dig og ikke sveket din pakt.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Vårt hjerte vek ikke tilbake, og våre skritt bøide ikke av fra din vei,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
så du skulde sønderknuse oss der hvor sjakaler bor, og dekke oss med dødsskygge.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Dersom vi hadde glemt vår Guds navn og utbredt våre hender til en fremmed gud,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
skulde Gud da ikke utforske det? Han kjenner jo hjertets skjulte tanker.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Men for din skyld drepes vi hele dagen, vi er regnet som slaktefår.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Våkn op! Hvorfor sover du, Herre? Våkn op, forkast ikke for evig tid!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Hvorfor skjuler du ditt åsyn, glemmer vår elendighet og vår trengsel?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For vår sjel er nedbøid i støvet, vårt legeme nedtrykt til jorden.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Reis dig til hjelp for oss, og forløs oss for din miskunnhets skyld!

< Zabura 44 >