< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Kumqondisi wokuhlabela. Ihubo lamaDodana kaKhora. Sizizwele ngezethu indlebe, yebo Oh Nkulunkulu obaba basitshela owakwenzayo ensukwini zabo, ensukwini zekadeni.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Ngezakho izandla wazixotsha izizwe wagxumeka obaba; wabahlifiza abantu wenza obaba baphumelela.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Kwakungasinkemba zabo ezathumba ilizwe, njalo kakusingalo yabo eyaletha ukunqoba; kwaba yisandla sakho sokunene, ingalo yakho, lokukhanya kobuso bakho, ngoba wawubathanda.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
UyiNkosi yami loNkulunkulu wami, ophayo ukunqoba kuJakhobe.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Ngawe siyazihlehlisa izitha zethu; ngebizo lakho siyazigxobagxoba izitha zethu.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Angilithembi idandili lami, inkemba yami kayingiletheli ukunqoba;
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
kodwa wena usipha ukunqoba phezu kwezitha zethu, abalwa lathi ubathela ihlazo.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Siyazincoma ngoNkulunkulu ilanga lonke, njalo sizalidumisa ibizo lakho nini lanini.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Kodwa manje ususilahlile wasiyangisa; kawusaphelekezeli izimpi zethu.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Wasenza sahlehla phambi kwesitha, abalwa lathi sebethethe impango.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Wasiyekela sadliwa njengezimvu wasichithachitha phakathi kwezizwe.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Wathengisa abantu bakho ngengcosana nje awazuza lutho ngalokho kuthengisa.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Ususenze saba lihlazo kubomakhelwane, inhlekisa lendumazo kwesihlalisene labo.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Ususenze saba yisiga phakathi kwezizwe; abantu banyikinya amakhanda ngathi.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Ukuyangeka kwami kuyangilandela ilanga lonke, ubuso bami buhuqwe ngehlazo,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
ngokuhozwa yilabo abangisolayo njalo abangenyanyayo, ngenxa yesitha esijonge ukuphindisela.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Konke lokhu kwenzakala kithi, lanxa sasingakulibalanga; asathembeka esivumelwaneni sakho.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Inhliziyo zethu zazingabuyelanga emuva; inyawo zethu zazingaphambukanga endleleni yakho.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Kodwa wasichoboza saba yikudla kwamaganyane, wasembesa ngomnyama omkhulu.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Aluba sasesilikhohliwe ibizo likaNkulunkulu wethu loba saphakamisela izandla zethu kunkulunkulu wezizweni,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
kambe ngabe uNkulunkulu kakubonanga lokho na, njengoba esazi imfihlo zenhliziyo?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Ikanti ngenxa yakho wena sikhangelane lokufa ilanga lonke; sithathwa njengezimvu ezizahlatshwa.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Vuka, Oh Thixo! Ulaleleni na? Ziphaphamise! Ungasilahli kokuphela.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Ubufihlelani ubuso bakho na, ukhohlwe ukuhlupheka kwethu lokuncindezelwa?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Sesibhuqwe phansi othulini; imizimba yethu isinamathele phansi.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Phakama usisize; sihlenge ngenxa yothando lwakho olungaphuthiyo.

< Zabura 44 >