< Zabura 44 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Eine Unterweisung der Kinder Korah, vorzusingen, Gott, wir haben mit unsern Ohren gehöret, unsere Väter haben uns erzählet, was du getan hast zu ihren Zeiten vor alters.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Du hast mit deiner Hand die Heiden vertrieben, aber sie hast du eingesetzt; du hast die Völker verderbet, aber sie hast du ausgebreitet.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Denn sie haben das Land nicht eingenommen durch ihr Schwert, und ihr Arm half ihnen nicht, sondern deine Rechte, dein Arm und das Licht deines Angesichts; denn du hattest Wohlgefallen an ihnen.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Gott, du bist derselbe mein König, der du Jakob Hilfe verheißest.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Durch dich wollen wir unsere Feinde zerstoßen; in deinem Namen wollen wir untertreten, die sich wider uns setzen.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Denn ich verlasse mich nicht auf meinen Bogen, und mein Schwert kann mir nicht helfen,
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
sondern du hilfst uns von unsern Feinden und machest zuschanden, die uns hassen.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Wir wollen täglich rühmen von Gott und deinem Namen danken ewiglich. (Sela)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Warum verstößest du uns denn nun und lässest uns zuschanden werden und zeuchst nicht aus unter unserm Heer?
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Du lässest uns fliehen vor unserm Feinde, daß uns berauben, die uns hassen.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Du lässest uns auffressen wie Schafe und zerstreuest uns unter die Heiden.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Du verkaufest dein Volk umsonst und nimmst nichts drum.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Du machst uns zur Schmach unsern Nachbarn, zum Spott und Hohn denen, die um uns her sind.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Du machst uns zum Beispiel unter den Heiden, und daß die Völker das Haupt über uns schütteln.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Täglich ist meine Schmach vor mir, und mein Antlitz ist voller Schande,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
daß ich die Schänder und Lästerer hören und die Feinde und Rachgierigen sehen muß.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Dies alles ist über uns kommen, und haben doch dein nicht vergessen, noch untreulich in deinem Bunde gehandelt;
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
unser Herz ist nicht abgefallen, noch unser Gang gewichen von deinem Wege,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
daß du uns so zerschlägest unter den Drachen und bedeckest uns mit Finsternis.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Wenn wir des Namens unsers Gottes vergessen hätten und unsere Hände aufgehoben zum fremden Gott,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
das möchte Gott wohl finden; nun kennet er ja unsers Herzens Grund.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Denn wir werden ja um deinetwillen täglich erwürget und sind geachtet wie Schlachtschafe.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Erwecke dich, HERR, warum schläfst du? Wache auf und verstoße uns nicht so gar!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Warum verbirgest du dein Antlitz, vergissest unsers Elends und Dranges?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Denn unsere Seele ist gebeuget zur Erde; unser Bauch klebet am Erdboden.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.