< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Pour la fin, aux fils de Coré pour l’intelligence. Ô Dieu, nous avons entendu de nos oreilles; nos pères nous ont annoncé L’œuvre que vous avez opéré dans leurs jours et dans des jours anciens.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Votre main a détruit entièrement des nations et établi nos pères; vous avez affligé des peuples et vous les avez chassés.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Car ce n’est point par leur glaive qu’ils se sont mis en possession d’une terre, et ce n’est point leur bras qui les a sauvés: Mais votre droite, et votre bras, et la lumière de votre visage, parce que vous vous êtes complu en eux.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
C’est vous qui êtes mon roi et mon Dieu: c’est vous qui décrétez les victoires de Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Avec vous, nous dissiperons nos ennemis par la force; et en votre nom, nous mépriserons ceux qui s’élèvent contre nous.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Car ce n’est pas en mon arc que j’espérerai: et mon glaive ne me sauvera pas.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
Car vous nous avez sauvés de ceux qui nous affligeaient, et vous avez confondu ceux qui nous haïssaient.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
C’est en Dieu que nous nous glorifierons tout le jour; et c’est votre nom que nous célébrerons à jamais.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Mais maintenant vous nous avez repoussés, et confondus; et vous ne sortirez pas à la tête de nos armées.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Vous nous avez fait tourner le dos à nos ennemis, et ceux qui nous haïssent arrachaient nos dépouilles.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Vous nous avez livrés comme des brebis que l’on mange, et vous nous avez dispersés parmi les nations.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Vous avez vendu votre peuple pour rien; et il n’y a pas eu une multitude d’acheteurs à leurs ventes.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Vous nous avez rendu un sujet d’opprobre à nos voisins, un objet d’insulte et de dérision à ceux qui sont autour de nous.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Vous nous avez fait la fable des nations et le secouement de tête des peuples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Tout le jour ma honte est devant moi, et la confusion de ma face m’a couvert entièrement,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
À la voix de celui qui m’adresse des reproches et qui m’invective, à la face de mon ennemi et de celui qui me persécute.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Tous ces maux sont venus sur nous et nous ne vous avons pas oublié, et nous n’avons pas iniquement agi contre votre alliance.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Et notre cœur ne s’est pas retiré en arrière; et vous avez détourné nos sentiers de votre voie.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Parce que vous nous avez humiliés dans un lieu d’affliction, l’ombre de la mort nous a enveloppés.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si nous avons oublié le nom de notre Dieu, et si nous avons étendu nos mains vers un Dieu étranger;
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Est-ce que Dieu ne s’en enquerra pas? Car il connaît, lui, les choses cachées du cœur.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Puisque, à cause de vous, nous sommes mis à mort tout le jour; nous sommes regardés comme des brebis de tuerie.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Levez-vous, pourquoi dormez-vous, Seigneur? Levez-vous, et ne nous rejetez pas pour toujours.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Pourquoi détournez-vous votre face, oubliez-vous notre misère et notre tribulation?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Car notre âme est humiliée dans la poussière, et notre ventre est collé à la terre.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Levez-vous, Seigneur, secourez-nous, et rachetez-nous à cause de votre nom.

< Zabura 44 >