< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Au maître chantre. Hymne des fils de Coré. O Dieu, nous avons ouï de nos oreilles, nos pères nous ont raconté les exploits que tu fis en leurs jours, aux jours d'autrefois.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
De ta main tu chassas les nations, pour les établir; tu détruisis les peuples, pour les multiplier.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Car ce ne fut pas par leur épée qu'ils conquirent le pays, ni leur bras qui les rendit vainqueurs, mais ta droite et ton bras, et la lumière de ta face; car tu leur fus propice.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
O Dieu! tu es mon Roi! Ordonne la délivrance de Jacob!
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Avec toi nous battons nos ennemis, par ton nom nous terrassons nos adversaires
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Car dans mon arc je ne me confie point, ce n'est pas mon épée qui me délivre;
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
mais c'est toi qui nous délivres de nos ennemis, et qui confonds ceux qui nous haïssent.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
De Dieu nous faisons gloire en tout temps, et nous louons éternellement ton nom. (Pause)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Cependant tu nous rejetas et nous couvris d'opprobre, et tu ne marchas plus avec nos armées;
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
tu nous fis reculer devant nos ennemis, et ceux qui nous haïssent, emportèrent des dépouilles;
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
tu nous livras comme la brebis que l'on mange, et parmi les nations tu nous disséminas;
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
tu vendis ton peuple à vil prix, et pour toi il n'eut pas une grande valeur;
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
tu nous exposas aux affronts de nos voisins, aux railleries et aux insultes de nos alentours;
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
tu nous fis passer en proverbe chez les nations, exciter des hochements de tête parmi les peuples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Toujours ma honte est devant mes yeux, et la confusion de ma face me couvre,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
à la voix de celui qui m'insulte et m'outrage, à l'aspect de l'ennemi et de l'homme hostile.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Tout cela nous est arrivé, et pourtant nous ne t'avions pas oublié, nous n'avions pas violé ton alliance,
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
notre cœur ne s'était point retiré de toi, et nos pas n'avaient pas dévié de tes voies,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
pour que tu nous écrases dans le pays des chacals, et que tu nous enveloppes d'une ombre de mort.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si nous avions oublié le nom de notre Dieu, et tendu nos mains vers un dieu étranger, est-ce que Dieu ne le pénétrerait pas,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
lui qui connaît les secrets de nos cœurs?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Mais non, pour toi nous sommes tués tous les jours, et regardés comme des brebis à égorger.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Veille! pourquoi dors-tu, Seigneur? Réveille-toi! ne nous rejette pas à jamais!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Pourquoi cacher ta face, oublier notre misère et notre oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Car jusqu'à la poussière notre âme est abattue, et notre corps à la terre est attaché.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Lève-toi! à notre secours! et sauve-nous pour l'amour de ta grâce.

< Zabura 44 >