< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Au chef des chantres. Par les fils de Coré. Maskîl. O Dieu! De nos oreilles nous l’avons entendue, nos pères nous l’ont racontée, l’œuvre que tu as accomplie de leurs jours, aux temps antiques.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Toi, de ta main, tu as dépossédé des nations, et tu les as implantés, eux; tu as ruiné des peuplades, et eux, tu les as multipliés.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Certes, ce n’est pas leur épée qui les a faits maîtres du pays, ni leur bras qui leur a donné la victoire: c’est ta droite, ton bras, la lumière de ta face; car tu les avais pris en affection.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
C’Est toi qui es mon roi, ô Dieu! Décrète les triomphes de Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Grâce à toi nous enfonçons nos ennemis, avec l’aide de ton nom, nous écrasons nos agresseurs.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Car je ne mets pas ma confiance en mon arc; ce n’est pas mon épée qui m’assure la victoire;
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
mais c’est toi qui nous fait triompher de nos ennemis, qui couvres de confusion ceux qui nous haïssent.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
En Dieu nous nous glorifions sans cesse, et à jamais nous célébrons ton nom. (Sélah)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Pourtant tu nous as rejetés et humiliés, et tu n’accompagnes plus nos armées.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Tu nous fais reculer devant l’ennemi: ceux qui nous haïssent pillent à leur aise.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Tu nous livres comme des troupeaux dont on se nourrit, et nous éparpilles parmi les nations.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Tu vends ton peuple à vil prix; tu n’estimes pas bien haut sa valeur.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Tu fais de nous un objet d’opprobre pour nos voisins, la risée et la moquerie de notre entourage.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Tu nous rends la fable des nations; nous excitons des hochements de tête parmi les peuples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Tout le temps, mon déshonneur est là, sous mes yeux, et mon visage se couvre de honte
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
à la voix de l’insulteur et du détracteur, à la vue de l’ennemi, avide de vengeance.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Tout cela nous est advenu, sans que nous t’ayons oublié, sans que nous ayons trahi ton alliance.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Notre cœur n’a pas rétrogradé, ni nos pas n’ont dévié de ton chemin,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
pour que tu dusses nous reléguer dans la région des monstres et nous recouvrir des ombres de la mort.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si nous avions oublié le nom de notre Dieu, étendu les mains vers un dieu étranger,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
est-ce que Dieu ne l’aurait pas constaté, puisqu’il connaît les secrets du cœur?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Mais pour toi nous subissons chaque jour la mort; on nous considère comme des brebis destinées à la boucherie.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Réveille-toi donc! Pourquoi demeures-tu endormi, Seigneur? Sors de ton sommeil, ne nous délaisse pas à jamais.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Pourquoi dérobes-tu ta face, oublies-tu notre misère et notre oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Car notre âme est abaissée jusque dans la poussière, notre corps est couché de son long sur le sol.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Lève-toi pour nous venir en aide, délivre-nous par un effet de ta bonté!

< Zabura 44 >