< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Au maître de chant. Des fils de Coré. Cantique. O Dieu, nous avons entendu de nos oreilles, nos pères nous ont raconté l’œuvre que tu as accomplie de leur temps, aux jours anciens.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
De ta main tu as chassé des nations pour les établir, tu as frappé des peuples pour les étendre.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Car ce n’est pas avec leur épée qu’ils ont conquis le pays, ce n’est pas leur bras qui leur a donné la victoire; mais c’est ta droite, c’est ton bras, c’est la lumière de ta face, parce que tu les aimais.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
C’est toi qui es mon roi, ô Dieu: ordonne le salut de Jacob!
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Par toi nous renverserons nos ennemis, en ton nom nous écraserons nos adversaires.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Car ce n’est pas en mon arc que j’ai confiance ce n’est pas mon épée qui me sauvera.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
Mais c’est toi qui nous délivres de nos ennemis, et qui confonds ceux qui nous haïssent.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
En Dieu nous nous glorifions chaque jour, et nous célébrons ton nom à jamais. — Séla.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Cependant tu nous repousses et nous couvres de honte; tu ne sors plus avec nos armées.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Tu nous fais reculer devant l’ennemi, et ceux qui nous haïssent nous dépouillent.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Tu nous livres comme des brebis destinées à la boucherie, tu nous disperses parmi les nations;
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
tu vends ton peuple à vil prix, tu ne l’estimes pas à une grande valeur.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Tu fais de nous un objet d’opprobre pour nos voisins, de moquerie et de risée pour ceux qui nous entourent.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Tu nous rends la fable des nations, et un sujet de hochements de tête parmi les peuples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Ma honte est toujours devant mes yeux, et la confusion couvre mon visage,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
à la voix de celui qui m’insulte et m’outrage, à la vue de l’ennemi et de celui qui respire la vengeance.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Tout cela nous arrive sans que nous t’ayons oublié, sans que nous ayons été infidèles à ton alliance.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Notre cœur ne s’est pas détourné en arrière, nos pas ne se sont pas écartés de ton sentier,
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
pour que tu nous écrases dans la retraite des chacals, et que tu nous couvres de l’ombre de la mort.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Si nous avions oublié le nom de notre Dieu, et tendu les mains vers un dieu étranger,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Dieu ne l’aurait-il pas aperçu, lui qui connaît les secrets du cœur?
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Mais c’est à cause de toi qu’on nous égorge tous les jours, qu’on nous traite comme des brebis destinées à la boucherie.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Réveille-toi! Pourquoi dors-tu, Seigneur? Réveille-toi, et ne nous repousse pas à jamais!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Pourquoi caches-tu ta face, oublies-tu notre misère et notre oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Car notre âme est affaissée jusqu’à la poussière, notre corps est attaché à la terre.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Lève-toi pour nous secourir, délivre-nous à cause de ta bonté!

< Zabura 44 >