< Zabura 44 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
For the chief musician. A psalm of the sons of Korah. A maschil. We have heard with our ears, God, our fathers have told us what work you did in their days, in the days of old.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
You drove out the nations with your hand, but you planted our people; you afflicted the peoples, but you spread our people out in the land.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For they did not obtain the land for their possession by their own sword, neither did their own arm save them; but your right hand, your arm, and the light of your face, because you were favorable to them.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
God, You are my King; command victory for Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Through you we will push down our adversaries; through your name we will tread them under, those who rise up against us.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For I will not trust in my bow, neither will my sword save me.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
But you have saved us from our adversaries, and have put to shame those who hate us.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
In God we have made our boast all the day long, and we will give thanks to your name forever. (Selah)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
But now you have thrown us off and brought us dishonor, and you do not go out with our armies.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
You make us turn back from the adversary; and those who hate us take spoil for themselves.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
You have made us like sheep to be slaughtered and have scattered us among the nations.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
You sell your people for nothing; you have not increased your wealth by doing so.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
You make us a rebuke to our neighbors, scoffed and mocked by those around us.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
You make us an insult among the nations, a shaking of the head among the peoples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
All the day long my dishonor is before me, and the shame of my face has covered me
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
because of the voice of him who rebukes and insults, because of the enemy and the avenger.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
All this has come on us; yet we have not forgotten you or dealt falsely with your covenant.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Our heart has not turned back; our steps have not gone from your way.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Yet you have severely broken us in the place of jackals and covered us with the shadow of death.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
If we have forgotten the name of our God or spread out our hands to a strange god,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
would not God search this out? For he knows the secrets of the heart.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Indeed, for your sake we are being killed all day long; we are considered to be sheep for the slaughter.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Awake, why do you sleep, Lord? Arise, do not throw us off permanently.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Why do you hide your face and forget our affliction and our oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For we have melted away into the dust; our bodies cling to the earth.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Rise up for our help and redeem us for the sake of your covenant faithfulness.