< Zabura 44 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
“To the chief musician, for the sons of Korach, a Maskil.” O God, with our ears have we heard, our fathers have told us, deeds which thou hadst done in their days, in times of old.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Thou, with thy hand, didst indeed drive out nations, and plant them; thou didst ill-treat people, and cause them to spread out.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For not by their sword did they obtain possession of the land, and their own arm brought them no victory; but thy right hand, and thy arm, and the light of thy countenance, because thou hadst given them thy favor.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Thou art my King, O God: ordain salvation for Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Through thee will we butt down our assailants: through thy name will we tread under foot our opponents.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For not in my bow will I trust, and my sword shall not help me.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
But thou helpest us against our assailants, and those that hate us thou puttest to shame.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Of God we boast all the day, and to thy name will we give thanks for ever. (Selah)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
But [now] thou hast cast off, and put us to the blush, and goest not forth with our armies.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Thou causest us to turn back from before our assailant: and they who hate us take spoil for themselves.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Thou givest us up like sheep for food, and among the nations hast thou dispersed us.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Thou sellest thy people for no value, and acquirest no gain by their price.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Thou renderest us a reproach to our neighbors, a scorn and a derision to those that are round about us.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Thou renderest us a by-word among the nations, a shaking of the head among the people.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
All the day is my disgrace before me, and the shame of my face covereth me;
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
Because of the voice of him that reproacheth and blasphemeth; by reason of the enemy and him that seeketh vengeance.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
All this is come over us, yet have we not forgotten thee; nor have we dealt falsely by thy covenant;
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Our heart is not moved backward, nor hath our step turned aside from thy path:
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Even when thou didst crush us in the abode of monsters, and cover us with the shadow of death.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
If we had forgotten the name of our God, or spread forth our hands to a strange God:
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Would not God search out this? for he knoweth the secrets of the heart.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
But for thy sake are we slain all the day; we are counted as flocks [destined] for slaughter.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Awake, wherefore wilt thou sleep, O Lord? arise, abandon us not for ever.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Wherefore wilt thou hide thy face, wilt thou forget our misery, and our oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For our soul is bowed down to the dust; our body cleaveth unto the earth.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Arise unto our help, and redeem us for the sake of thy kindness.