< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Unto the end, for the sons of Core, to give understanding. We have heard, O God, with our ears: our fathers have declared to us, The work, thou hast wrought in their days, and in the days of old.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Thy hand destroyed the Gentiles, and thou plantedst them: thou didst afflict the people and cast them out.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For they got not the possession of the land by their own sword: neither did their own arm save them. But thy right hand and thy arm, and the light of thy countenance: because thou wast pleased with them.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Thou art thyself my king and my God, who commandest the saving of Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Through thee we will push down our enemies with the horn: and through thy name we will despise them that rise up against us.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For I will not trust in my bow: neither shall my sword save me.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
But thou hast saved us from them that afflict us: and hast put them to shame that hate us.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
In God shall we glory all the day long: and in thy name we will give praise for ever.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
But now thou hast cast us off, and put us to shame: and thou, O God, wilt not go out with our armies.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Thou hast made us turn our back to our enemies: and they that hated us plundered for themselves.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Thou hast given us up like sheep to be eaten: thou hast scattered us among the nations.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Thou hast sold thy people for no price: and there was no reckoning in the exchange of them.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Thou hast made us a reproach to our neighbours, a scoff and derision to them that are round about us.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Thou hast made us a byword among the Gentiles: a shaking of the head among the people.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
All the day long my shame is before me: and the confusion of my face hath covered me,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
At the voice of him that reproacheth and detracteth me: at the face of the enemy and persecutor.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
All these things have come upon us, yet we have not forgotten thee: and we have not done wickedly in they covenant.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
And our heart hath not turned back: neither hast thou turned aside our steps from thy way.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
For thou hast humbled us in the place of affliction: and the shadow of death hath covered us.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
If we have forgotten the name of our God, and if we have spread forth our hands to a strange god:
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Shall not God search out these things: for he knoweth the secrets of the heart.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Because for thy sake we are killed all the day long: we are counted as sheep for the slaughter.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Arise, why sleepest thou, O Lord? arise, and cast us not off to the end.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Why turnest thou face away? and forgettest our want and our trouble?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For our soul is humbled down to the dust: our belly cleaveth to the earth.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Arise, O Lord, help us and redeem us for thy name’s sake.

< Zabura 44 >