< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
To the chief Musician. Of the sons of Korah. An instruction. O God, with our ears have we heard, our fathers have told us, the work thou wroughtest in their days, in the days of old:
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Thou, by thy hand, didst dispossess the nations, but them thou didst plant; thou didst afflict the peoples, but them didst thou cause to spread out.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For not by their own sword did they take possession of the land, neither did their own arm save them; but thy right hand, and thine arm, and the light of thy countenance, because thou hadst delight in them.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Thou thyself art my king, O God: command deliverance for Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Through thee will we push down our adversaries; through thy name will we tread them under that rise up against us.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For I will not put confidence in my bow, neither shall my sword save me.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
For thou hast saved us from our adversaries, and hast put them to shame that hate us.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
In God will we boast all the day, and we will praise thy name for ever. (Selah)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
But thou hast cast off, and put us to confusion, and dost not go forth with our armies;
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Thou hast made us to turn back from the adversary, and they that hate us spoil for themselves;
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Thou hast given us over like sheep [appointed] for meat, and hast scattered us among the nations;
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Thou hast sold thy people for nought, and hast not increased [thy wealth] by their price;
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Thou makest us a reproach to our neighbours, a mockery and a derision for them that are round about us;
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Thou makest us a byword among the nations, a shaking of the head among the peoples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
All the day my confusion is before me, and the shame of my face hath covered me,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
Because of the voice of him that reproacheth and blasphemeth; by reason of the enemy and the avenger.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
All this is come upon us; yet have we not forgotten thee, neither have we dealt falsely against thy covenant:
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Our heart is not turned back, neither have our steps declined from thy path;
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Though thou hast crushed us in the place of jackals, and covered us with the shadow of death.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
If we had forgotten the name of our God, and stretched out our hands to a strange god,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Would not God search this out? for he knoweth the secrets of the heart.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
But for thy sake are we killed all the day long; we are reckoned as sheep for slaughter.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Awake, why sleepest thou, Lord? arise, cast [us] not off for ever.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Wherefore hidest thou thy face, [and] forgettest our affliction and our oppression?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For our soul is bowed down to the dust; our belly cleaveth unto the earth.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Rise up for our help, and redeem us for thy loving-kindness' sake.

< Zabura 44 >