< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Unto the end. To the sons of Korah, toward understanding. We have heard, O God, with our own ears. Our fathers have announced to us the work that you wrought in their days and in the days of antiquity.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Your hand dispersed the Gentiles, and you transplanted them. You afflicted a people, and you expelled them.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
For they did not take possession of the land by their sword, and their own arm did not save them. But your right hand and your arm, and the light of your countenance did so, because you were pleased with them.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
You yourself are my king and my God, who commands the salvation of Jacob.
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
With you, we will brandish a horn before our enemies; and in your name, we will spurn those rising up against us.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
For I will not hope in my bow, and my sword will not save me.
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
For you have saved us from those who afflict us, and you have bewildered those who hate us.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
In God, we will give praise all day long; and in your name, we will confess forever.
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
But now, you have rejected and bewildered us, and you will not go forth with our armies, O God.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
You have turned our back to our enemies, and those who hated us have plundered for themselves.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
You have given us over like sheep for food. You have scattered us among the Gentiles.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
You have sold your people without a price, and no great number was exchanged for them.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
You have set us as a disgrace to our neighbors, a scoff and a derision to those who are around us.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
You have set us as a parable among the Gentiles, a shaking of the head among the peoples.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
All day long my shame is before me, and the confusion of my face has covered me,
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
before the voice of the reproacher and the commentator, before the face of the adversary and the pursuer.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
All these things have come upon us, yet we have not forgotten you, and we have not acted unjustly in your covenant.
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
And our heart has not turned back. And you have not diverted our steps from your way.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
For you humbled us in a place of affliction, and the shadow of death has covered us.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
If we have forgotten the name of our God, and if we have extended our hands to a foreign god,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
will not God find this out? For he knows the secrets of the heart.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
For, because of you, we are being killed all day long. We are considered as sheep for the slaughter.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Rise up. Why do you fall asleep, O Lord? Rise up, and do not reject us in the end.
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Why do you turn your face away, and why do you forget our needfulness and our tribulation?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
For our soul has been humbled into the dust. Our belly has been bound to the earth.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Rise up, O Lord. Help us and redeem us, because of your name.

< Zabura 44 >