< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Rends-moi justice, ô Dieu, défends ma cause Contre une nation infidèle! Délivre-moi de l'homme trompeur et pervers!
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
Tu es mon Dieu, mon rempart. Pourquoi m'as-tu rejeté? Pourquoi dois-je marcher en vêtements de deuil, Sous l'oppression de l'ennemi?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
Envoie ta lumière et ta vérité: qu'elles me guident; Qu'elles me ramènent sur ta montagne sainte. Dans ta demeure!
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
Alors je m'avancerai vers l'autel de Dieu, » Du Dieu qui est ma joie et mon allégresse. Puis je te célébrerai sur la harpe, ô Dieu, mon Dieu!
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Pourquoi t'abats-tu, mon âme, et pourquoi frémis-tu en moi? Espère en Dieu, car je le célébrerai encore: Il est mon salut et mon Dieu!

< Zabura 43 >