< Zabura 43 >
1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Fais-moi justice, ô Dieu, et défends ma cause contre une nation infidèle! Délivre-moi de l'homme trompeur et pervers!
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
Car tu es le Dieu de ma force. Pourquoi m'as-tu rejeté? Pourquoi marcherai-je en deuil, sous l'oppression de l'ennemi?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
Envoie ta lumière et ta vérité; qu'elles me conduisent, qu'elles m'amènent sur ta montagne sainte, vers tes tabernacles!
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
Et j'entrerai vers l'autel de Dieu, vers Dieu, ma joie et mon allégresse; et je te louerai avec la harpe, ô Dieu, mon Dieu!
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Pourquoi t'abats-tu, mon âme, et pourquoi frémis-tu en moi? Attends-toi à Dieu, car je le louerai encore; il est mon salut et mon Dieu!