< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Juge-moi, ô Dieu! et prends en main ma cause contre une nation sans piété; délivre-moi de l’homme trompeur et inique.
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
Car toi, ô Dieu! tu es ma force; pourquoi m’as-tu rejeté? Pourquoi marché-je en deuil à cause de l’oppression de l’ennemi?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
Envoie ta lumière et ta vérité: elles me conduiront, elles m’amèneront à ta montagne sainte et à tes demeures.
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
Et je viendrai à l’autel de Dieu, au Dieu de l’allégresse de ma joie; et je te célébrerai sur la harpe, ô Dieu, mon Dieu!
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Pourquoi es-tu abattue, mon âme? et pourquoi es-tu agitée au-dedans de moi? Attends-toi à Dieu; car je le célébrerai encore: il est le salut de ma face et mon Dieu.

< Zabura 43 >