< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
God, declare that I (am innocent/have not done things that are wrong). Defend me when (ungodly people/people who do not worship you) say things against me, rescue me from people who deceive and [say things about me that are] not true.
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
You are God, the one who protects me; (why have you abandoned me?/it seems that you have abandoned me!) [RHQ] It does not seem right that [RHQ] I am forced to mourn/cry constantly because my enemies are cruel to me.
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
Shine your light on me and speak your truth to me; and let them guide me, and take me back to Zion, your sacred hill [at Jerusalem], and to [your temple], where you live.
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
When you do that, I will go to your altar, to [worship you], my God, who causes me to be extremely joyful. There I will praise you, the God whom I [worship], while I play my harp.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
So (why am I sad and discouraged?/I should not be sad and discouraged!) [RHQ] I confidently expect God [to bless me], and I will praise him again, my God, the one who saves me.

< Zabura 43 >