< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Judge me, O God, and plead my cause against an ungodly nation: from the deceitful and unjust man do thou deliver me.
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
For thou art the God of my fortress: why hast thou abandoned me? why must I walk about grieved, under the oppression of the enemy?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
Send thou thy light and thy truth, these shall guide me; they shall bring me unto thy holy mountain, and to thy dwellings:
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
That I may go unto the altar of God, unto God the joy of my gladness; and that I may thank thee upon the harp, O God, my God.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Why art thou cast down, O my soul? and why art thou disquieted within me? Hope thou in God; for I shall yet thank him, the salvation of my countenance, and my God.

< Zabura 43 >