< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Be Thou my judge, O God, and plead my cause against an ungodly nation; O deliver me from the deceitful and unjust man.
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
For Thou art the God of my strength; why hast Thou cast me off? Why go I mourning under the oppression of the enemy?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
O send out Thy light and Thy truth; let them lead me; let them bring me unto Thy holy mountain, and to Thy dwelling-places.
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
Then will I go unto the altar of God, unto God, my exceeding joy; and praise Thee upon the harp, O God, my God.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Why art thou cast down, O my soul? and why moanest thou within me? Hope thou in God; for I shall yet praise Him, the salvation of my countenance, and my God.

< Zabura 43 >