< Zabura 43 >

1 Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Be my judge, O God, supporting my cause against a nation without religion; O keep me from the false and evil man.
2 Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
You are the God of my strength; why have you put me from you? why do I go in sorrow because of the attacks of my haters?
3 Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
O send out your light and your true word; let them be my guide: let them take me to your holy hill, and to your tents.
4 Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
Then I will go up to the altar of God, to the God of my joy; I will be glad and give praise to you on an instrument of music, O God, my God.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Why are you crushed down, O my soul? and why are you troubled in me? put your hope in God, for I will again give him praise who is my help and my God.

< Zabura 43 >