< Zabura 42 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
Njengalokhu indluzele inxwanele izifula zamanzi, ngokunjalo umphefumulo wami unxwanela wena, Nkulunkulu.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
Umphefumulo wami womela uNkulunkulu, uNkulunkulu ophilayo. Ngizafika nini ngibonakale phambi kobuso bukaNkulunkulu?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Inyembezi zami beziyikudla kwami emini lebusuku, lapho besithi kimi usuku lonke: Ungaphi uNkulunkulu wakho?
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
Ngikhumbula lezizinto ngathulula umphefumulo wami phakathi kwami, ngoba ngadlula lexuku, ngaya labo endlini kaNkulunkulu ngelizwi lentokozo lendumiso, ixuku eligubha umkhosi.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Udanelani mphefumulo wami? Ukhathazekelani phakathi kwami? Themba kuNkulunkulu, ngoba ngisezamdumisa, ngosizo lobuso bakhe.
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
Nkulunkulu wami, umphefumulo wami udanile phakathi kwami; ngakho ngizakukhumbula ngiselizweni leJordani lelamaHermoni, ngisentabeni iMizari.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Inziki ibiza inziki ekuhlokomeni kwezimpophoma zakho; wonke amagagasi akho lamaza akho adlule phezu kwami.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
Emini iNkosi izalaya uthandolomusa wayo, lebusuku ingoma yayo izakuba lami; umkhuleko wami kuNkulunkulu wempilo yami.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
Ngizakuthi kuNkulunkulu, idwala lami: Ungikhohlweleni? Ngihambelani ngikwezimnyama ngenxa yocindezelo lwesitha?
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Njengokuchoboza emathanjeni ami, izitha zami ziyangiklolodela, lapho zisithi kimi usuku lonke: Ungaphi uNkulunkulu wakho?
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Udaneleni mphefumulo wami? Njalo ukhathazekelani phakathi kwami? Themba kuNkulunkulu, ngoba ngisezamdumisa, usindiso lobuso bami, loNkulunkulu wami.

< Zabura 42 >