< Zabura 42 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
Pour le chef musicien. Une contemplation par les fils de Korah. Comme le cerf s'impatiente devant les ruisseaux, ainsi mon âme se languit de toi, Dieu.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
Mon âme a soif de Dieu, du Dieu vivant. Quand vais-je venir me présenter devant Dieu?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Mes larmes ont été ma nourriture jour et nuit, alors qu'ils me demandent sans cesse: « Où est ton Dieu? »
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
Je me souviens de ces choses, et je répands mon âme en moi, comment j'avais l'habitude d'aller avec la foule, et de les conduire à la maison de Dieu, avec la voix de la joie et de la louange, une multitude célébrant un jour saint.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Pourquoi es-tu désespéré, mon âme? Pourquoi es-tu troublé en moi? L'espoir en Dieu! Car je le louerai encore pour l'aide salvatrice de sa présence.
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
Mon Dieu, mon âme est désespérée au-dedans de moi. C'est pourquoi je me souviens de toi depuis le pays du Jourdain, les hauteurs de l'Hermon, de la colline Mizar.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Deep appelle à Deep au bruit de vos chutes d'eau. Toutes tes vagues et tous tes flots m'ont balayé.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
L'Éternel commandera sa bonté pendant le jour. Dans la nuit, sa chanson sera avec moi: une prière au Dieu de ma vie.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
Je demanderai à Dieu, mon rocher: « Pourquoi m'as-tu oublié? Pourquoi suis-je en deuil à cause de l'oppression de l'ennemi? »
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Comme une épée dans mes os, mes adversaires m'outragent, alors qu'ils me demandent sans cesse: « Où est ton Dieu? »
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Pourquoies-tu désespéré, mon âme? Pourquoi es-tu troublé en moi? Espère en Dieu! Car je le louerai encore, l'aide salvatrice de mon visage, et mon Dieu.

< Zabura 42 >