< Zabura 42 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
To the choirmaster a poem of [the] sons of Korah. Like a deer [which] it pants towards channels of water so being my it pants to you O God.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
It thirsts being my - for God for [the] God living when? will I go and I may appear? [the] presence of God.
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
It has been of me tear[s] my food by day and night when say to me all the day where? [is] God your.
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
These [things] I will remember - and I will pour out on myself - soul my that I passed on - with the crowd I led them to [the] house of God with [the] sound of a shout of joy and thanksgiving a multitude celebrating a festival.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why? are you bowed down - O soul my and were you in turmoil? on me wait for God for again I will give thanks to him [the] salvation of presence his.
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
O God my on me being my it is bowed down there-fore I will remember you from [the] land of [the] Jordan and Hermon from mount Mizar.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Deep to deep [is] calling to [the] sound waterfalls your all breakers your and waves your over me they have passed.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
By day - he commands Yahweh - covenant loyalty his and in the night (song his *Q(K)*) [is] with me a prayer to [the] God of life my.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
I will say - to God rock my why? have you forgotten me why? mourning do I walk in [the] oppression of an enemy.
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
With a shattering - in bones my they have taunted me opposers my when say they to me all the day where? [is] God your.
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why? are you bowed down - O soul my and why? are you in turmoil on me wait for God for again I will give thanks to him [the] salvation of face my and God my.

< Zabura 42 >