< Zabura 42 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
For the music director. A psalm (maskil) of the sons of Korah. As a deer longs for flowing streams, so I long for you, God.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
I am thirsty for God, the living God. When can I go and see God's face?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
My tears have been my only food, day and night, while people ask me all day long, “Where is your God?”
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
I am crushed as I remember how I walked with the crowds, leading them in a procession to the house of God, with shouts of joy and songs of thanks among the worshipers at the festival.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why am I so discouraged? Why do I feel so sad? I will hope in God; I will praise him because he is the one who saves me—
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
my God! Even though I am very discouraged, I still remember you: from the land of Jordan and Hermon, and from Mount Mizar.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
You thunder through the raging waters, through the noise of the waterfalls. Your crashing waves surge over me—I feel like I'm drowning.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
But every day the Lord shows me his trustworthy love; every night he gives me songs to sing—a prayer to the God of my life.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
I cry out, “My God, my rock, why have you forgotten me? Why must I go around weeping because of the attacks of my enemies?”
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
The mocking of my attackers crushes my bones. They're always asking me, “Where is your God?”
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why am I so discouraged? Why do I feel so sad? I will hope in God; I will praise him because he is the one who saves me—my God!

< Zabura 42 >