< Zabura 42 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
As the hart pants after the water brooks, so my soul pants after thee, O God.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
My soul thirsts for God, for the living God. When shall I come and appear before God?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
My tears have been my food day and night, while they continually say to me, Where is thy God?
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
These things I remember, and pour out my soul within me, how I went with the throng, and led them to the house of God, with the voice of joy and praise, a multitude keeping holyday.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why are thou cast down, O my soul? And why are thou disquieted within me? Hope thou in God, for I shall yet praise him for the help of his countenance.
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
O my God, my soul is cast down within me. Therefore I remember thee from the land of the Jordan, and the Hermons, from the hill Mizar.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Deep calls to deep at the noise of thy waterfalls. All thy waves and thy billows have gone over me.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
Yet Jehovah will command his loving kindness in the daytime, and in the night his song shall be with me, even a prayer to the God of my life.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
I will say to God my rock, Why have thou forgotten me? Why do I go mourning because of the oppression of the enemy?
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
As with a sword in my bones, my adversaries reproach me; while they continually say to me, Where is thy God?
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Why are thou cast down, O my soul? And why are thou disquieted within me? Hope thou in God, for I shall yet praise him, the help of my countenance, and my God.