< Zabura 42 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
Zborovođi. Poučna pjesma. Sinova Korahovih. Kao što košuta žudi za izvor-vodom, tako duša moja čezne, Bože, za tobom.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
Žedna mi je duša Boga, Boga živoga: o, kada ću doći i lice Božje gledati?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Suze su kruh moj danju i noću, dok me svednevice pitaju: “Gdje ti je Bog tvoj?”
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
Duša moja gine kada se spomenem kako koračah u mnoštvu predvodeć' ih k Domu Božjem uz radosno klicanje i hvalopojke u povorci svečanoj.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Što si mi, dušo, klonula i što jecaš u meni? U Boga se uzdaj, jer opet ću ga slaviti, spasenje svoje, Boga svog!
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
Tuguje duša u meni, stoga se tebe spominjem iz zemlje Jordana i Hermona, s brda Misara.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Bezdan doziva bezdan bukom slapova tvojih: sve vode tvoje i vali preko mene prijeđoše.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
Nek' mi danju Jahve naklonost udijeli, a noću pjesmom ću hvalit' Boga života svog.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
Reći ću Bogu: “Hridino moja, zašto me zaboravljaš? Zašto obilazim žalostan, pritisnut dušmanima?”
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Kosti mi se lome od poruge neprijatelja dok me svednevice pitaju: “Gdje ti je Bog tvoj?”
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Što si mi, dušo, klonula i što jecaš u meni? U Boga se uzdaj, jer opet ću ga slaviti, spasenje svoje, Boga svog!

< Zabura 42 >