< Zabura 41 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Načelniku godbe, psalm Davidov. Blagor mu, kdor se spominja siromaka, govoreč: O času nadloge bode ga otél Gospod.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Gospod ga bode rešil, ohranil življenju; srečen bode na zemlji, in ne izdajaj ga želji sovražnikov njegovih.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Gospod naj ga podpira na postelji slabosti: vse ležišče njegovo vsled bolezni njegove preméni,
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Ko govorim: Gospod, milost mi stóri, ozdravi dušo mojo, ker tebi sem grešil.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Sovražniki moji so slabo govorili o meni: Kdaj bode umrl in bode izginilo ime njegovo?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Ko je tedaj prihajal obiskat me kdó, govorilo je laž srce njegovo; zbiralo si je krivico: šel je ven in právil.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Vkup so šepetali zoper mene vsi sovražniki moji; zoper mene so izmišljali, kar bi mi bilo v zlo, govoreč:
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Stvar silno malopridna tiči v njem globoko, in ker leži, več ne vstane.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Tudi mož, ki je živel v miru z menoj, v katerega sem zaupal, kateri je jedel mojo jed, vzdignil je peto proti meni.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Ti pa, Gospod, storí mi milost, in zbúdi me, da jim povrnem.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.