< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Til sangmesteren; en salme av David. Salig er den som akter på den elendige; på den onde dag skal Herren frelse ham.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Herren skal verge ham og holde ham i live; han skal bli lykksalig i landet, og du skal visselig ikke overgi ham til hans fienders mordlyst.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Herren skal understøtte ham på sykesengen; hele hans leie forvandler du i hans sykdom.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Jeg sier: Herre, vær mig nådig, helbred min sjel! for jeg har syndet imot dig.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mine fiender taler ondt om mig: Når skal han dø, og hans navn forgå?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Og dersom en kommer for å se til mig, taler han falske ord; hans hjerte samler sig ondskap; han går ut og taler derom.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Alle de som hater mig, hvisker sammen imot mig; de optenker imot mig det som er mig til skade:
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
En ugjerning henger ved ham, og han som ligger der, skal ikke stå op mere.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Også den mann som jeg hadde fred med, som jeg stolte på, som åt mitt brød, har løftet sin hæl imot mig.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Men du, Herre, vær mig nådig og hjelp mig op! Så vil jeg gjengjelde dem.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
Derpå kjenner jeg at du har behag i mig, at min fiende ikke skal fryde sig over mig.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Og mig holder du oppe i min uskyld og setter mig for ditt åsyn evindelig.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Lovet være Herren, Israels Gud, fra evighet og til evighet! Amen, amen.

< Zabura 41 >