< Zabura 41 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Dāvida dziesma. Dziedātāju vadonim. Svētīgs tas, kas nabagu apgādā; to Tas Kungs izglābs ļaunā dienā.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Tas Kungs to pasargās un uzturēs pie dzīvības, Viņš tam liks labi klāties virs zemes un to nenodos viņa ienaidnieku prātam.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Tas Kungs to atspirdzinās uz neveselības gultas; Tu viņam palīdzēsi guļā no visas viņa sērgas.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Es sacīju: ak Kungs, esi man žēlīgs, dziedini manu dvēseli, jo es pret Tevi esmu grēkojis.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mani ienaidnieki runā ļaunu no manis: kad viņš nomirs un viņa vārds ies bojā?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Un kad tie nāk, mani apraudzīt, tad tie viltu runā; ar savu sirdi tie sameklē niekus, iziet ārā un izplukšķ.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Visi, kas mani ienīst, musina kopā pret mani, un domā ļaunu pret mani.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Blēņu darbu tie apņēmušies savā prātā: kad tas guļ, tad viņš vairs necelsies!
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Un pat mans draugs, kam es uzticējos, kas manu maizi ēda, mani min pa kājām.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Bet Tu, ak Kungs, esi man žēlīgs, un uzcel mani, tad es tiem to maksāšu!
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
Pie tam es zinu, ka Tev labs prāts pie manis, ka mans ienaidnieks par mani negavilēs.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Bet Tu mani uzturi manā nenoziedzībā, un mani iecel Savā priekšā mūžīgi.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Slavēts lai ir Tas Kungs, Israēla Dievs, mūžīgi mūžam! Āmen, Āmen.