< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
In finem. Psalmus ipsi David. [Beatus qui intelligit super egenum et pauperem: in die mala liberabit eum Dominus.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Dominus conservet eum, et vivificet eum, et beatum faciat eum in terra, et non tradat eum in animam inimicorum ejus.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Dominus opem ferat illi super lectum doloris ejus; universum stratum ejus versasti in infirmitate ejus.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Ego dixi: Domine, miserere mei; sana animam meam, quia peccavi tibi.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Inimici mei dixerunt mala mihi: Quando morietur, et peribit nomen ejus?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Et si ingrediebatur ut videret, vana loquebatur; cor ejus congregavit iniquitatem sibi. Egrediebatur foras et loquebatur.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
In idipsum adversum me susurrabant omnes inimici mei; adversum me cogitabant mala mihi.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Verbum iniquum constituerunt adversum me: Numquid qui dormit non adjiciet ut resurgat?
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Etenim homo pacis meæ in quo speravi, qui edebat panes meos, magnificavit super me supplantationem.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Tu autem, Domine, miserere mei, et resuscita me; et retribuam eis.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
In hoc cognovi quoniam voluisti me, quoniam non gaudebit inimicus meus super me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Me autem propter innocentiam suscepisti; et confirmasti me in conspectu tuo in æternum.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Benedictus Dominus Deus Israël a sæculo et usque in sæculum. Fiat, fiat.]

< Zabura 41 >